![cover image](https://wikiwandv2-19431.kxcdn.com/_next/image?url=https://upload.wikimedia.org/wikipedia/commons/thumb/3/35/International_leaders_sign_joint_statement_at_COP26_%252851649202102%2529_%2528Suluhu_crop%2529.jpg/640px-International_leaders_sign_joint_statement_at_COP26_%252851649202102%2529_%2528Suluhu_crop%2529.jpg&w=640&q=50)
Samia Suluhu Hassan
Shugaban Kasar Tanzaniya / From Wikipedia, the free encyclopedia
Samia Suluhu Hassan (an haife ta a ranan 27 Janairu 1960) 'yar siyasar Tanzaniya ce wacce ke aiki a matsayin shugabar Tanzaniya ta shida kuma a yanzu. Ita mamba ce a jam'iyyar Social-Democrat Chama Cha Mapinduzi (CCM). Suluhu ita ce shugabar gwamnati mace ta uku a wata kasa ta Gabashin Afirka (EAC), bayan Sylvie Kinigi a Burundi da Agathe Uwilingiyimana a Ruwanda, kuma ita ce shugabar mace ta farko a Tanzaniya. Ta fara aiki a ranar 19 ga Maris 2021 bayan mutuwar Shugaba John Magufuli a ranar 17 ga Maris 2021.
![]() | |||||||
---|---|---|---|---|---|---|---|
![]() | |||||||
19 ga Maris, 2021 - ← John Magufuli (en) ![]()
5 Nuwamba, 2015 - 19 ga Maris, 2021 ← Mohamed Gharib Bilal (en) ![]()
Nuwamba, 2010 - ga Yuli, 2015 District: Makunduchi (en) ![]() | |||||||
Rayuwa | |||||||
Haihuwa |
Makunduchi (en) ![]() | ||||||
ƙasa | Tanzaniya | ||||||
Harshen uwa | Harshen Swahili | ||||||
Karatu | |||||||
Makaranta |
University of Manchester (en) ![]() The Open University of Tanzania (en) ![]() Mzumbe University (en) ![]() Southern New Hampshire University (en) ![]() Lumumba Secondary School (en) ![]() | ||||||
Harsuna |
Turanci Harshen Swahili | ||||||
Sana'a | |||||||
Sana'a | ɗan siyasa da Mai tattala arziki | ||||||
Kyaututtuka |
gani
| ||||||
Imani | |||||||
Addini | Musulunci | ||||||
Jam'iyar siyasa |
Party of the Revolution (en) ![]() |
Yar asalin Zanzibar Suluhu ta yi minista a yankin mai cin gashin kansa a lokacin gwamnatin shugaba Amani Karume. Ta taba zama ‘yar majalisa mai wakiltar mazabar Makunduchi daga shekarar 2010 zuwa 2015 sannan ta kasance ministar kasa a ofishin mataimakin shugaban kasa kan harkokin kungiyar daga 2010 zuwa 2015. A shekarar 2014, an zabe ta a matsayin mataimakiyar shugabar majalisar mazabar da ke da alhakin tsara sabon kundin tsarin mulkin kasar.
![Thumb image](http://upload.wikimedia.org/wikipedia/commons/thumb/3/32/Samia_Suluhu_Hassan_%2834538118495%29.jpg/640px-Samia_Suluhu_Hassan_%2834538118495%29.jpg)
Suluhu ta zama mace ta farko a matsayin mataimakiyar shugaban kasar Tanzaniya bayan babban zaben shekarar 2015, bayan an zabe ta a kan tikitin CCM tare da shugaba Magufuli. An sake zaben Suluhu da Magufuli a karo na biyu a shekarar 2020. Ta yi aiki a matsayin shugabar rikon kwarya mace ta biyu a cikin EAC a takaice - shekaru 27 bayan Sylvie Kinigi ta Burundi, wanda ya kai kusan karshen shekara ta 1993.