![cover image](https://wikiwandv2-19431.kxcdn.com/_next/image?url=https://upload.wikimedia.org/wikipedia/commons/thumb/e/e4/Mimiko_Closeup.jpg/640px-Mimiko_Closeup.jpg&w=640&q=50)
Olusegun Mimiko
From Wikipedia, the free encyclopedia
Olusegun Mimiko ( Yoruba;) an haife shi ranar 3 ga watan Oktoba na shekarar 1954, shi ne dan takarar sanata na Zenith Labour Party a Ondo ta Tsakiya a zaben shekarar 2019.[1]Shi ɗan siyasan Nijeriya ne wanda ya yi aiki na 16, kuma na biyar a farar hula, Gwamnan Jihar Ondo, Nijeriya, daga watan Fabrairu shekarar 2009, zuwa Fabrairu shekarar 2017. Gwamna na farko a zango biyu na jihar Ondo kuma gwamna na farkon Jam’iyyar Labour a Najeriya. Mimiko ya taba zama ministan tarayya na gidaje da, sakataren gwamnatin jihar Ondo, sannan ya taba zama kwamishinan lafiya na jihar Ondo sau biyu. Ya ci gaba da sha'awar siyasa tun yana ƙaramin. dan siyasa ya fara ne a makarantar likitanci a Jami'ar Ife (yanzu Obafemi Awolowo University), inda ya kasance memba na Majalisar Wakilai ta (Majalisar) kuma ya yi aiki a matsayin jami'in hulda da jama'a na kungiyar International Students’ Association of the institution daga shekarar 1977 zuwa shekara ta 1978.
![]() | |||
---|---|---|---|
![]() | |||
ga Faburairu, 2009 - ga Faburairu, 2017 ← Olusegun Agagu (en) ![]() | |||
Rayuwa | |||
Haihuwa | 3 Oktoba 1954 (69 shekaru) | ||
ƙasa | Najeriya | ||
Ƙabila | Yarbawa | ||
Harshen uwa | Yarbanci | ||
Karatu | |||
Makaranta |
Jami'ar Obafemi Awolowo (1972 - 1976) | ||
Harsuna |
Turanci Yarbanci Pidgin na Najeriya | ||
Sana'a | |||
Sana'a | ɗan siyasa | ||
Imani | |||
Addini | Kiristanci | ||
Jam'iyar siyasa | Nigeria Labour Party |
Bayan kammala karatunsa a jami'a a shekarar 1980 kuma ya kammala National Youth Service Corp, Mimiko ya fara aikin likita. A cikin 1985, ya kafa MONA MEDICLINIC a cikin garin Ondo wanda yayi aiki a matsayin cibiyar taimakon al'umma. [2]
Nadin Mimiko na siyasa na farko shi ne kwamishina na kiwon lafiya da walwala da jin dadin jama'a a jihar Ondo daga shekarar 1992 zuwa shekara ta 1993 lokacin da wani juyin mulkin soja ya kawo karshen mulkin dimokiradiyya ta Uku . Bayan dawowar mulkin dimokiradiyya a Najeriya, Mimiko ya sake zama kwamishinan lafiya a jihar Ondo daga shekarar 1999 zuwa shekara ta 2002.
A shekarar 2003, aka nada shi sakataren Gwamnatin Jihar Ondo (SSG). Ya rike wannan mukamin har zuwa watan Yulin shekarar 2005, lokacin da aka nada shi a matsayin ministan gidaje da ci gaban birane na tarayya. [2] Mimiko ya yi murabus daga mukaminsa na ministan tarayya don ya yi takarar gwamnan Ondo da mai ci, Olusegun Agagu a zaben shekarar 2007 .[3]
![Thumb image](http://upload.wikimedia.org/wikipedia/commons/thumb/6/63/Olusegun_Mimiko.jpg/640px-Olusegun_Mimiko.jpg)
Mimiko ya lashe zaben. Amma, tasirin tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa ta sanar da Agagu a matsayin wanda ya yi nasara. Mimiko ya kalubalanci sakamakon zaben a kotuna kan abin da ya kasance rikicin shekaru biyu na shari’a wanda ya kawo karshen bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaben na gwamna ta hanyar hukuncin daya yanke na Kotun, da kuma Kotun daukaka kara a shekarar 2009.[4] [5]Ya ci gaba da sake lashe zaben a shekarar 2012, inda ya doke babban abokin karawarsa, Olusola Oke na Jam’iyyar Democratic Party.
A lokacin mulkin Mimiko a matsayin gwamna, sauye-sauyen da ya yi a bangaren kiwon lafiya, ilimi, ci gaban al'umma, sabunta birane da kuma amfani da fasaha a harkokin mulki sun samu karbuwa a kasashe na duniya.[6][7][8][9][10][11][12]
Bayan ya bar ofis, Mimiko ya kwashe shekara guda yana gabatar da laccocin jama'a tare da yin kira kan kiwon lafiyar duniya da kyakkyawan shugabanci a Najeriya, London, da Washington DC.[13][14]
A watan Satumba na shekarar 2018, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasar Najeriya a zaben shekarar 2019.[15]Ya amshi takara a matsayin dan takarar shugaban kasa na Labour Zenith Party a watan Oktoba, shekarar 2018.[16]A ranar 14 ga watan Nuwamba, shekarar 2018, Mimiko ya sanar da cewa ya dakatar da yakin neman zabensa na shugaban kasa, 'yan kwanaki kafin a bude kakar yakin neman zabe a hukumance. Ya dauki tikitin takarar sanata na Zenith Labour Party na mazabar tarayya ta Ondo ta Tsakiya.[17] Mimiko a halin yanzu yana zaune a Ondo City,a mahaifar sa.