From Wikipedia, the free encyclopedia
Alhaji Sa'idu Barda ɗan siyasar Najeriya ne wanda aka zaɓe shi a dandalin jam'iyyar Republican National Republican Convention (NRC) a matsayin gwamnan jihar Katsina, Nigeria, mai rike da muƙami tsakanin watan Janairu shekarar (1992) zuwa Nuwamban shekara ta (1993) a lokacin jamhuriya ta uku ta Najeriya. Ya ci gaba da taka rawar gani a siyasa a jamhuriya ta hudu ta Najeriya.[1]
Saidu Barda | |||
---|---|---|---|
ga Janairu, 1992 - Nuwamba, 1993 ← John Madaki - Emmanuel Acholonu → | |||
Rayuwa | |||
ƙasa | Najeriya | ||
Harshen uwa | Hausa | ||
Karatu | |||
Harsuna |
Turanci Hausa Pidgin na Najeriya | ||
Sana'a | |||
Sana'a | ɗan siyasa | ||
Imani | |||
Jam'iyar siyasa | Babban taron jam'iyyar Republican |
Barda ya kammala aikin ginin masakar fulawa a Katsina, wanda aka fara shi a shekarar 1981, amma daga baya aka yi watsi da shi. A cikin watan Yuni a shekara ta1993, Barda ya kafa wani kwamiti a kan Gyaran Ilimi "don duba lalacewar ilimi a makarantu da kuma samar da mafita." Ya kuma aza harsashin ginin Othman Dan Fodio Institute, wanda aka yi niyyar ta zama jami’ar Musulunci ta farko a Najeriya amma daga baya aka yi watsi da ita.[2]
A zaɓen gwamnan jihar Katsina a watan Disamba a shekara ta (1991) Barda ya doke Umaru Yar'Adua, ɗan takarar jam'iyyar Social Democratic Party (SDP). Daga baya 'Yar'Adua ya ci gaba da zama shugaban kasa a watan Afrilun shekara ta (2007).[3] Kanin Umaru Janar Shehu 'Yar'aduwa, wanda a lokacin fitaccen ɗan siyasa ne da ke da muradin zama shugaban ƙasa, ya kasa bayar da cikakken goyon bayansa ga neman Umaru. Barda ya samu tagomashi daga shugaban ƙasa na mulkin soja a lokacin, Janar Ibrahim Babangida.[4]
Barda ya goyi bayan soke zaɓen da Babangida ya yi a ranar 12 ga watan Yunin shekarar (1993) na zaben MKO Abiola a matsayin shugaban ƙasa, yana mai cewa "jini zai rika zubowa a sikelin da ba a taba ganin irinsa ba" idan har za a sauya soke zaɓen[5] Gwagwarmayar siyasar da ta biyo bayan sokewar ta kai ga juyin mulkin da Janar Sani Abacha ya yi a watan Nuwamba a shekara ta (1993) inda aka kori dukkan zaɓaɓɓun gwamnoni.
Barda ya taka rawar gani a siyasa a jamhuriya ta hudu ta Najeriya, inda ya zama shugaban jam'iyyar United Nigeria People's Party (UNPP). A watan Janairun shekara ta (2003) a matsayinsa na shugaban babban taron jam’iyyar UNPP, Barda ya bayyana cewa Sanata Jim Ifeanyichukwu Nwobodo ne zai zama ɗan takarar jam’iyyar a zaɓen shugaban kasa na Afrilu a shekara ta (2003).[6] A watan Mayun shekarar (2003) Barda ya kasance memba a kungiyar shawarwari ta Arewa, ƙungiyar shugabannin siyasar Arewa. A watan Oktoban shekara ta (2009) Barda yana wani taro inda tsohon shugaban ƙasa na mulkin soja Muhammadu Buhari ya sanar da kafa sabuwar kawancen siyasa, wato National Democratic Movement.[7][8] A shekara ta (2010) Barda ya kasance mataimakin shugaban kungiyar tuntuba ta Arewa.[9]
Seamless Wikipedia browsing. On steroids.
Every time you click a link to Wikipedia, Wiktionary or Wikiquote in your browser's search results, it will show the modern Wikiwand interface.
Wikiwand extension is a five stars, simple, with minimum permission required to keep your browsing private, safe and transparent.