![cover image](https://wikiwandv2-19431.kxcdn.com/_next/image?url=https://upload.wikimedia.org/wikipedia/commons/thumb/3/31/Flag_of_Burkina_Faso.svg/langha-640px-Flag_of_Burkina_Faso.svg.png&w=640&q=50)
Kungiyar Kwallon Kafa ta Mata ta Burkina Faso
From Wikipedia, the free encyclopedia
Kungiyar kwallon kafa ta mata ta Burkina Faso, tana wakiltar Burkina Faso a wasan kwallon kafa ta duniya na mata. Hukumar kwallon kafa ta Burkinabe ce ke tafiyar da ita. [1] Ta buga wasanta na farko a ranar 2 ga Satumba, shekara ta 2007 a Ouagadougou da Nijar kuma ta yi nasara da ci 10-0, sakamako mafi kyau har yau. Wasanta na gaba sune Nijar (5-0) da Mali (2-4).
![]() | |
---|---|
![]() | |
Bayanai | |
Iri |
women's national association football team (en) ![]() |
Ƙasa | Burkina Faso |
Mulki | |
Mamallaki |
Fédération Burkinabé de Football (en) ![]() |
A wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin mata ta Afirka ta shekarar 2014 da Ghana, Burkina Faso ta yi rashin nasara da ci 6-0 a jimillar. Tuni Tunisiya ta doke ta da ci 2-0 a jimillar kwallaye a gasar neman gurbin shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka ta mata na 2016 . An tashi kunnen doki da Burkina Faso da Gambia a gasar neman gurbin shiga gasar ta 2018 da aka tashi 3-3 da jumulla; Gambia ta ci 5-3 a bugun fenariti.
Tawagar kwallon kafar mata ta Burkina Faso ta buga wasanta na gida a filin wasa na Stade du 4 Août.