![cover image](https://wikiwandv2-19431.kxcdn.com/_next/image?url=https://upload.wikimedia.org/wikipedia/commons/thumb/f/f8/Nigeria_Federal_Capital_Territory_map.png/640px-Nigeria_Federal_Capital_Territory_map.png&w=640&q=50)
Harin bam a Nyanya, Afrilu 2014
Harin ƴan ƙungiyar Boko Haram a Najeriya / From Wikipedia, the free encyclopedia
A ranar 14 ga watan Afrilu, 2014 da misalin ƙarfe 6:45 na safe, wasu bama-bamai biyu sun tashi a wata tashar mota mai cunkoson jama’a, a garin Nyanya na Jihar Nasarawa, hakan ya jawo mutuwar mutane aƙalla 88 tare da jikkata wasu 200. Tashar motar na da nisan kilomita 8 ne daga kudu maso yammacin babban birnin tarayya.[1][2][3][4][5]
Quick Facts Iri, Bangare na ...
![]() | ||||
| ||||
Iri |
bomb attack (en) ![]() Kisan Kiyashi | |||
---|---|---|---|---|
Bangare na | Rikicin Boko Haram | |||
Kwanan watan | 14 ga Afirilu, 2014 | |||
Wuri | New Nyanya | |||
Ƙasa | Najeriya | |||
Adadin waɗanda suka rasu | 75 | |||
Adadin waɗanda suka samu raunuka | 124 |
Kulle
Kungiyar Boko Haram ta ɗauki alhakin kai harin kwanaki shida bayan faruwar lamarin. Hakan ya faru ne sa'o'i kaɗan kafin a sace ƴan matan Chibok.