Tarzoma mai nasaba da addini a Najeriya From Wikipedia, the free encyclopedia
Rikicin Jos na shekara ta 2008 ya kasance tarzoma ce da ta shafi kiristoci da musulmi dangane da sakamakon zaben kananan hukumomi da aka gudanar a ranakun 28 da 29 ga watan Nuwamba 2008 a garin Jos dake yankin Middle Belt a Najeriya.[1][2] Rikicin na kwanaki biyu ya yi sanadin jikkata ɗaruruwa, yayin da aƙalla mutane 761 suka mutu.[3] An tura sojojin Najeriya (a yankin).[4]
Ma’aikatan zaɓe dai ba su fito fili sun bayyana sunayen waɗanda suka yi nasara a zaɓen ba, sai aka fara yada jita-jitar cewa ɗan takarar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Barista Timothy Gyang Buba ne ya lashe zaɓen,[5] ya doke ɗan takarar jam’iyyar All Nigerian Peoples Party. Jama’ar al’ummar Hausawa Musulmi, sun fara gudanar da zanga-zanga tun kafin a fitar da sakamakon, wanda ya haifar da arangama da ta yi sanadiyar mutuwar daruruwan mutane tsakanin Musulmi da Kirista, wadanda suka fi goyon bayan Buba.[6]
Irin wannan tarzoma da aka yi a shekarar 2001 tsakanin Kirista da Musulmi a Jos ma ta yi sanadiyyar mutuwar ɗaruruwan mutane.[7] Rikicin 2004 a Yelwa, wani gari a Jihar Filato ya haifar da abin da ake kira Kisan Yelwa. Fadan da aka yi a jihar Kaduna ta arewa ta tsakiya a lokacin da aka yi yunƙurin kafa shari’ar Musulunci a shekarar 2000, ya haifar da raba garin Kaduna. Hakan ya biyo bayan tarzomar Kaduna a watan Nuwamban shekarar 2002, sakamakon yadda Najeriya ta karbi bakuncin gasar Miss World, wadda daya daga cikin wadanda suka fafata ta lashe gasar a bara.[8]
Rikicin na kwanaki biyu ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutane 761,[3] sai kuma gidaje, masallatai, coci-coci da makarantu sun lalace ko an kona su.[9][10] Ƙungiyar agaji ta Red Cross ta Najeriya ta bayar da rahoton cewa mutane 10,000 ne suka tsere daga gidajensu saboda tarzomar,[2][11] kuma suna zaune a matsugunan da gwamnati ta samar na wucin gadi.[6] An tura sojojin Najeriya cikin birnin domin magance rikicin, gami da shiga a tsakanin Kiristoci da Musulmai.[12] An soke tashin jirage izuwa Jos, an kuma toshe hanyoyin arewa.[13]
Jonah Jang, gwamnan jihar Filato, ya sanya dokar hana fita ta sa'o'i 24 a gundumomi hudu na birnin, kuma an ba sojoji damar "harbi" don hana sake afkuwar tashin wata tarzomar.[6] hukumar Human Rights Watch ta yi zargin cewa sojoji da ƴan sanda sun yi kisan gilla fiye da 130 a lokacin da suke mayar da martani kan tarzomar.[9] An kama matasa da yawa ɗauke da makamai na dukkan bangarorin biyu-(musulmai da kiristoci) a shingayen titin sojoji.[12] Ƴan sanda sun ce an kama sama da mutane 500 sakamakon tarzomar. Sai dai jami'an jihar sun ce babu wanda aka samu nasarar gurfanar da shi a gaban kuliya.[3]
Seamless Wikipedia browsing. On steroids.
Every time you click a link to Wikipedia, Wiktionary or Wikiquote in your browser's search results, it will show the modern Wikiwand interface.
Wikiwand extension is a five stars, simple, with minimum permission required to keep your browsing private, safe and transparent.