Kungiyar kwallon kafa ta Mali
From Wikipedia, the free encyclopedia
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙasar Mali ( Faransa: Équipe de football du Mali ) tana wakiltar ƙasar Mali a gasar ƙwallon ƙafa ta duniya kuma tana ƙarƙashin hukumar kula da wasan ƙwallon ƙafa ta ƙasar Mali . Laƙabin ƙungiyar shi ne Les Aigles. Suna wakiltar dukkanin FIFA da Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF).
Yayin da ƙasar Mali ta kasance babbar ƙasa ta matasa a nahiyar Afirka da ma duniya baki ɗaya, ba ta taɓa samun damar shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA ba a tarihi. Sau 12 sun samu tikitin shiga gasar cin kofin Afrika .
FIFA ta dakatar da Mali a ranar 17 ga watan Maris shekarar 2017 saboda katsalandan da gwamnati ta yi wa hukumar ƙwallon ƙafar ƙasar, wato rusa kwamitin zartarwa. Sai dai hukumar ta FIFA ta sake dawo da bangaren a ranar 29 ga watan Afrilu bayan da gwamnatin Mali ta sake gabatar da kwamitin zartarwa.[1]