Birnin oman
From Wikipedia, the free encyclopedia
Kasar Oman ƙasa ce ta Larabawa dake yammacin yankin Asiya. Tana kudu maso gabashin gabar tekun Larabawa, kuma ta ratsa bakin Tekun Fasha. Oman na da iyaka kasa da kasar Saudiyya, Daular Larabawa (Dubai), da Yemen, a lokaci guda tayi iyaka ta ruwa iyakokin teku da Iran da Pakistan. Tekun Larabawa ne ke kudu maso gabas, da Gulf of Oman a arewa maso gabas. Daular Madha da Musandam na kewaye da Hadaddiyar Daular Larabawa a kan iyakokinsu, tare da mashigin Hormuz (wanda ke da alaƙa da Iran) da mashigin tekun Oman sun kafa iyakokin Musandam. Muscat shine babban birnin ƙasar kuma birni mafi girma.[1]
Daga karni na 17, Omani Sultanate wata daula ce, tana fafatawa da daulolin Fotigal da Birtaniyya don yin tasiri a Tekun Farisa da Tekun Indiya. A lokacin da yake kololuwa a cikin karni na 19, tasirin Omani da iko ya mamaye mashigin Hormuz zuwa Iran da Pakistan, har zuwa kudu da Zanzibar.[2]A cikin karni na 20, sultanate ya zo ƙarƙashin rinjayar Burtaniya. Sama da shekaru 300, dangantakar da aka gina tsakanin masarautun biyu ta ginu ne bisa moriyar juna. Birtaniya ta amince da mahimmancin yankin Oman a matsayin cibiyar kasuwanci da ke tabbatar da hanyoyin kasuwancinsu a cikin Tekun Farisa da Tekun Indiya tare da kare daularsu a yankin Indiya. A tarihi, Muscat ita ce babbar tashar kasuwanci ta yankin Gulf Persian. Oman cikakkiyar masarauta ce wacce wani Sultan ke jagoranta. Qaboos bin Said shi ne Sultan daga 1970 har zuwa rasuwarsu a ranar 10 ga Janairu, 2020.[3]Qaboos wanda ya rasu bai haihu ba, ya bayyana sunan dan uwansu Haitham bin Tariq a matsayin magajinsa a wata wasika, kuma iyalan sun tabbatar da su a matsayin Sarkin Oman. "Haitham bin Tariq sworn in as Oman's new sultan". Al Jazeera.[4]
A hukumance,, Oman ita ce kasa mafi tsufa mai cin gashin kanta a cikin kasashen Larabawa.[5][6]Mamba ce ta Majalisar Dinkin Duniya, kungiyar kasashen Larabawa, kungiyar hadin kan kasashen yankin Gulf, kungiyar masu rajin kare hakkin bil adama da kungiyar hadin kan musulmi. Tana da ajiyar mai a matsayi na 22 a duniya[7][8] A shekarar 2010, shirin ci gaban Majalisar Dinkin Duniya ya sanya Oman a matsayin kasa mafi ci gaba a duniya a cikin shekaru 40 da suka gabata.[9] Wani ɓangare na tattalin arzikinta ya haɗa da yawon shakatawa da cinikin kifi, dabino da sauran amfanin gona. Oman ta kasance cikin kasashe masu babban tattalin arziki ta hanyar samun manyan kudin shiga, a shekarar 2022, Oman ta zama 64th mafi zaman lafiya a duniya bisa ga bisa ga kididdigar Zaman Lafiya ta Duniya.[10]