Haƙƙin Ɗan Adam a Norway
From Wikipedia, the free encyclopedia
Haƙƙoƙin ɗan adam a Norway suna kare ainihin haƙƙoƙin kowane mutum a cikin Mulkin Norway . Ana kiyaye waɗannan haƙƙoƙin ta Babi na E na Kundin Tsarin Mulki na Norway ko Kongeriket Norges Grunnlov, da kuma amincewa da wasu yarjejeniyoyin ƙasa da ƙasa da Majalisar Dinkin Duniya ta sauƙaƙe . Ƙasar tana da sadaukar da kai ga haƙƙin ɗan adam kuma ita ce ƙasa ta biyu da ta amince da yarjejeniyar Turai kan haƙƙin ɗan adam .
![]() | ||||
---|---|---|---|---|
human rights by country or territory (en) ![]() | ||||
Bayanai | ||||
Ƙasa | Norway | |||
Wuri | ||||
|
IKo da yake ana kallon Norway a matsayin mai taka-tsan-tsan a harkokin haƙƙin ɗan adam, inda take matsayi na farko a cikin kididdigar ci gaban ɗan adam ta shirin raya ƙasa na Majalisar Dinkin Duniya a shekaru 12 cikin shekaru 15 da suka wuce, har yanzu batutuwan haƙƙin ɗan adam suna tasowa. Batun da ya fi yaduwa a cikin tarihin baya-bayan nan shi ne gwagwarmayar neman yancin kasa ta ' yan asalin Sami, a karkashin barazanar gwamnatin Norway da ke amfani da yankin Sápmi don albarkatun kasa.[1] [2][3]